Connect with us

News

Hisbah Ta Fara Binciken Matar Da Ta Auri Saurayin Ƴarta A Kano

Published

on

DAGA KHADIJA NASEER MUSA 

 

Advertisement

 

Babban kwamandan hukumar Hisbah Sheikh Harun Ibn Sina ya ce ya kafa wani kwamiti domin gudanar da bincike game da zargin da ake yi wa wata mata a jihar na kashe aurenta tare da auren saurayin ƴarta.

Advertisement

 

Iyayen matar ne dai suka yi ƙorafin cewar shugaban Hisbah na ƙaramar hukumar Rano ya aurar da ƴar tasu ba tare da izininsu ba.

Advertisement

An saki magoya bayan Arsenal da aka kama kan wasansu da Manchester United

“Kwanaki biyu da suka gabata ne labari ya iso teburina cewa wata mata ta kashe aurenta, inda kuma ta auri saurayin ƴarta, saboda haka nan take na kafa kwamiti domin yin bincike game da batun”.

 

Advertisement

“Mun gayyato duka ɓangarorin da lamarin ya shafa”.

 

Advertisement

“Kuma da zarar kwamitin ya kammala bincike za mu sanar wa duniya halin da ake ciki”

 

Advertisement

Babban kwamanda Hisbah na Kano ya kuma ce wannan labari ne mai rikirtawa da ba su taɓa ganin irin sa ba.

 

Advertisement

”Duk da cewa muna samun matsaloli masu yawa a kowace rana, to amma a tsawon lokacin da na kwashe a matsayin kwamandan hukumar, wannan shi ne karo na farko da na samu labari makamncin wannan, hakan bai taɓa faruwa ba”, in ji Ibn Sina.

 

Advertisement

Yadda lamarin ya faru

Kawun matar, mai suna Abdullahi Musa Rano ne ya fara gabatar da ƙorafin ranar Litinin da daddare a gidan Radiyon Freedom da ke jihar Kano, inda ya zargi shugaban Hisba na ƙaramar hukumar Rano da aurar da ƴarsu ga saurayin ƴarta, bayan ta kashe aurenta da mijinta.

Advertisement

 

Abdullahi ya ce abin da ya faru abin kunya ne ga danginsu, kuma abu ne da ba za su bari ya kasance ba.

Advertisement

 

“Ta takura wa mijinta har sai da ya sake ta, domin ta auri wannan mutumin. wannan abin kunya ne ga danginmu, domin haka muke kira ga kwamandan hukumar Hisbah da gwamnatin jihar Kano da su duba wannan batu”.

Advertisement

 

Wani mazaunin ƙaramar hukumar Rano mai suna Sabiu Sani wanda kuma ya san labarin ya shaida wa BBC cewa tabbas yarinyar ta ƙi amincewa da soyayyar saurayin nata duk kuwa da ƙoƙarin da ya yi na jan hankalinta.

Advertisement

 

“Matar na ganin cewa a maimakon ita da ƴar tata su yi biyu babu a kan mutumin da take ganin cewa mutumin kirki ne, shi ya sa ta ga cewar ya kamata ita ta aure shi, tun da ita ƴar tata ba ta son sa”.

Advertisement

 

“Abin da ya faru abu ne mai rikitarwa don haka ne mutane ke ta maganar a ko’ina a cikin garinmu a daidai wannan lokaci.”

Advertisement

 

Sabi’u ya ce a yanzu ba su san inda ma’auratan suke ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending