News
Kanin tsohon Shugaban Kasa ’Yar’aduwa ya lashe kujerar Sanata a Katsina
Abdulaziz Musa ’Yar’aduwa, kane ga tsohon Shugaban Kasa, Umaru Musa ’Yar’aduwa, ya lashe kujerar Sanatan Katsina ta Tsakiya a karkashin jam’iyyar APC.
INEC ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben bayan ya samu kuri’a 153,512, yayin da Aminu Sirajo na PDP ya sami kuri’a 152,140.
Sai dai wakilan jam’iyyar PDP sun ki amincewa da sakamakon a wajen tattara shi.
Advertisements
