News
Gwamnatin Taraba Ta Kafa Kwamitin Yaki Da Hako Ma’adanai Ba bisa Ka’ida Ba
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnatin jihar Taraba ta kaddamar da kwamitin mutane 17 domin aiwatar da dokar hana hako ma’adanai ba bisa ka’ida ba da kuma sarewa da sarrafa wasu bishiyoyi ba tare da izini ba kamar su African Rosewood
Sakataren gwamnatin jihar, Gebon Kataps, wanda ya wakilci gwamna Agbu Kefas a wajen kaddamar da kwamitin a ranar Asabar, ya ce matakin aiwatar da dokar ya samo asali ne daga rahotannin tsaro da gwamnatin jihar ta samu.
Hukumar NSCDC Ta Ceto Wata Mata Da Mahaifinta Ya Garkameta A Daki Tsawon Shekaru 5
Ya kuma bukaci mambobin sashin da su sanya dokar hana noman itacen fulawa a cikin shirinsu na gudanar da ayyukansu.
Gidan talabijan channels ya rawaito cewa, ayyukan masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba ya haifar da babbar barazana ga yanayin muhalli.
