News
Yan Bindiga Sun Kashe Masu Gadi jihar Benue
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wasu ‘yan bindiga sun kashe jami’an ‘yan banga da ke karkashin hukumar sa kai ta jihar Benue (BSCVG), Saater Apera.
A cewar shugaban karamar hukumar Logo, Salome Tor, an kashe Apera ne lokacin da ‘yan bindiga suka yi wa ‘yan kungiyar BSCVG kwanton bauna tare da bude musu wuta.
Gwamnatin Taraba Ta Kafa Kwamitin Yaki Da Hako Ma’adanai Ba bisa Ka’ida Ba
Daily trust ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a daren Juma’a a kauyen Tse Anwhwan da ke kan titin Iorza – Jootar yayin da ma’aikatan ke dawowa daga ofishin ‘yan sanda na Ugba da ke karamar hukumar Logo.
Tor ya bayyana cewa, “A ranar 30 ga watan Yuni, 2023 da misalin karfe 8 na dare, ‘yan bindiga dauke da makamai sun kai hari ga ‘yan kungiyar BSCVG a Tse Anwhwan a kan titin Iorza zuwa Jootar yayin da suke dawowa daga hedikwatar ‘yan sanda ta Ugba, inda suka dauki wani mai laifi da aka kama da rago sata.
“Sun yi kwanton bauna ne suka bude wuta kan wadanda aka kashe tare da kashe Mista Saater Apera. Sun kuma harbe Mista Bartholomew tare da raunata daya. ‘Yan bindigar sun kuma kwace babur din Bajaah (BM100) mallakar BSCVG a gundumar UK/Tswarev.
Shugaban karamar hukumar ya kara da cewa sauran wadanda suka jikkata a yanzu haka suna karbar magani a wata cibiyar lafiya da ke karamar hukumar da ke kauyen Iorza a Logo.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Benue, SP Catherine Anene, ba ta amsa kira ko sakon da aka yi ta wayar tarhonta ba.
