News
Rundunar Yan Sanda Sun Gano Wasu Shanu Da Suka Bace A Kano.
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta gano wasu shanu da ba a tantance adadinsu ba da ke yawo a unguwar Ranka Hotoro da ke karamar hukumar Tarauni a jihar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Rundunar sandan jahar kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya rabawa manema labarai a Kano ranar Lahadin nan.
Kiyawa ya ce, wani mutumin kirki ne ya ga shanun da suka bace a ranar 13 ga watan Yuli kuma ya ja hankalin ofishin rundunar ‘yan sanda na Hotoro.
mutum ya shaida wa ’yan sanda cewa a kan hanyarsa ta zuwa Rakat Hotoro Quarters Kano, ya ga wasu shanu suna yawo sama da sa’o’i uku.
“Bayan samun rahoton, an tuntubi mazauna yankin kuma an kokarin gano masu shanun wanda hakan ya ci tura,” in ji shi.
Hakazalika sanarwar ta ce a ranar 14 ga Yulin 2023, wani mutum ya ba da rahoton ganin wata jaka wadda ake kyautata zaton ta fasinja ce da ya dauko a cikin baburin adaidaita sahu.
“An kai rahotan ne ofishin ‘yan sanda na Hotoro kuma duk kokarin da aka yi na gano mai ita lamarin ya ci tura,” in ji shi.
Jaridar DailyNigerian ta rawaito cewa Sanarwar ta shawarci mazauna garin Kano da ke neman neman dukiyoyin da suka bata da su ziyarci ofishin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, a shedikwatar ‘yan sandan Kano, tare da shaidar mallakarsu.
NAN
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
