Sports
An dakatar da Paul Pogba kan zargin shan kayan kara kuzari
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
An dakatar da dan wasan Juventus da Faransa Paul Pogba daga kwallon kafa bayan an gano yana shan abubuwan kara kuzari.
“Kungiyar kwallon kafa ta Juventus ta sanar a yau Litinin, 11 ga watan Satumba, 2023, cewa Paul Labile Pogba ya karbi takardar dakatarwa daga kotun yaki da shan kayan kara kuzari bayan gwajin da aka yi masa ranar 20 ga watan Agusta,” in ji kungiyar.
“Kungiyar tana da damar yin nazari kan mataki na gaba,” a cewar sanarwar.
An dakatar da Pogba ne bayan Juventus ta doke Udinese ranar 20 ga watan Agusta a wasan da aka bar shi a benci.
Pogba, wanda ya lashe Kofin Duniya a 2018, shi ne dan wasa mafi tsada lokacin da ya bar Juventus zuwa Manchester United a 2016. United ta biya €105m ($116.4m) domin sayen Pogba daga Juventus.
Ya taimaka wa Manchester United wajen cin Kofin UEFA Europa na 2017.
A 2022, Pogba ya sake komawa Juventus amma ba kasafai yake buga wasa ba sakamakon raunukan da yake fama da su.
A wani labarin kuma An Yi Holin Kwamishinan ‘Yan Sandan Bogi, da Wasu Mutane 12
Gwamnan jahar Ondo, Rotimi Akeredolu ya dawo gida Najeriya bayan dogon hutun da ya dauka domin duba lafiyarsa a kasar Jamus.
Gwamnan ya bar Najeriya watanni ukku da suka gabata domin duba lafiyarsa a kasar ta Jamus.
Shugaban masu rinjaye a zauren majalisar dokokin jihar Ondo, Wole Ogunmolasuyi, wanda ya tabbatar da dawowar gwamnan ga wakilinmu, Ya ce a yanzu haka gwamnan yana gidansa dake birnin Badun.
Kazalika maid akin gwamnan, Uwargida Betty ta tabbatar da dawowar mai gidan nata a shafinta na X, inda ta wallafa hotonsa a cikin jirgin sama.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
