News
Da Ɗumi Ɗuminsa! Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da ɗan majalisar tarayya na NNPP a Kano
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Kotun Daukaka ƙara dake zaman ta a birnin tarayya Abuja, ta tabbatar wa da ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙaramar hukumar Tarauni Hon Mukhtar Umar Yarima na jam’iyyar NNPP kujerar sa.
Abba Kabir Yusuf ya kafa hujja 43 kan zaɓen Kano a ƙarar da ya ɗaukaka
Wanda a baya dai Ɗan majalisar tarayya na ƙaramar hukumar Tarauni Hon Hafizu kawu na jam’iyyar APC ya kalubalanci zaɓen da aka gudanar a kotun sauraren kararrakin zaɓe a jihar kano.
Advertisements
