Connect with us

News

Dole ne Cibiyoyin Lafiya Masu Zaman Kansu Subi ƙa’idoji  – Prof. Salisu

Published

on

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA

 

Advertisement

An shawarci cibiyoyin tantance masu zaman kansu da ke jihar Kano da su bi ka’idojin da aka gindaya Musu na gudanar da ayyukansu kamar yadda dokar Hukumar Kula da Lafiya Masu Zaman Kansu ta jahar Kano PHIMA ta tanada ko kuma a rufe su.

Shugaban Hukumar Kula da Lafiya Masu Zaman Kansu (PHIMA), Farfesa Salisu Ahmad Ibrahim ne ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi bayan rufe wata cibiyar Al-Sultan Diagnostic Laboratory da ke titin kotu, Gyadi-Gyadi.

Advertisement

kashi 80 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar mashako ba su yi allurar rigakafi ba -Dr Faisal Shu’aibu

Farfesa Salisu ya bayyana cewa chibiyar ta kara ayyukan da suke yi fiye da yadda aka basu takardar shedar aiwatar war su.

A cewarsa, “Mun je ne domin mu kula da cibiyar, wanda hakan na daga cikin umarnin da aka ba mu na mu tsallaka wurin sosai domin tabbatar da cewa ta cika dukkan bukatun da ake bukata, abin bakin ciki, mun gano cewa sun ci gaba da gudanar da ayyukansu ba tare da saninmu ba.

Advertisement

 

Shugaban hukumar ya ci gaba da cewa hakan ne ya sanya hukumar ta PHIMA rufe cibiyar saboda rashin cika ka’idojin da ake bukata, inda ya kara da cewa cibiyar za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai sun cika dukkan ka’idojin da dokokin hukumar suka shimfida da suka hada da karfin ma’aikata, ayyukan da suka gindaya.

Advertisement

 

Daga nan sai Farfesa Salisu ya yi kira ga duk cibiyoyin bincike masu zaman kansu da ke aiki a jihar da su tabbatar sun bi dokokin da suka kafa PHIMA da kuma ka’idojin gudanar da aiki, inda ya bayyana cewa babbar manufar hukumar ita ce ta kare rayukan al’ummar jihar. kuma ba za a iya cimma hakan ba sai an bi tsarin da ya dace.

Advertisement

 

Daga nan sai ya yi kira ga cibiyoyin lafiya masu zaman kansu da su ba hukumarsa hadin kai domin ciyar da harkokin kiwon lafiyar jihar yadda ake so, yana mai cewa ba za a amince da gudanar da ayyukan da ba bisa ka’ida ba a kowace cibiyar kiwon lafiya ta jihar Kano.

Advertisement

Ya kuma yabawa kwamishinan lafiya Dr. Abubakar Labaran Yusuf bisa irin kwazonsa da goyon baya ga matakai da matakan da hukumar ta PHIMA ke dauka na tsaftace ayyukan cibiyoyin kiwon lafiya masu zaman kansu a jihar, ya kuma yabawa ma’aikatan hukumar bisa jajircewa da suka yi. a yayin gudanar da ayyukan hukumar.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending