News
Hatsarin Tirela Ya Yi Ajalin Mutum 25 A Jihar Neja
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wata tirela da ke ɗauke da kusan mutum 230 a cikinta ta yi hatsari a Jihar Neja, inda akalla mutum 25 suka rasu nan take.
Bayanai sun nuna motar ta yi hatsarin ne ita kaɗai a kauyen Takalafiya da ke kan babbar hanyar Yawuri a Karamar Hukumar Magama ta Jihar Neja.
Dan majalisar Ghana ya nemi afuwar Harry Maguire kan zolayar da ya yi masa a bara
A cewar Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar, Bologi Ibrahim, Gwamnan Jihar, Mohammed Umar Bago, ya damu matuka da hatsarin sannan ya bukaci direbobi su daina karya dokokin tuki.
Ya ce hatsarin, wanda aka yi ranar Talata ya faru ne sakamakon gudun wuce sa’a, wanda ya sa motar ta ƙwace daga hannun direbanta.
Bayanai sun nuna tirelar dai ta taso ne daga Jihar Sakkwato dauke da mutum 229, wadanda suka hada da maza da mata da kananan yara a cikinta.
Rahotanni sun ce nan take mutum 25 suka mutu, yayin da wasu da dama suka samu munanan raunuka kuma yanzu aka garzaya da su Babban Asibitin Kontagora, inda suke samun kulawa.
Kazalika, wadanda suka rasu yanzu haka an kai gawarwakinsu dakin adana gawarwaki na asibitin na Kontagora.
A wani labarin kuma Dan majalisar Ghana ya nemi afuwar Harry Maguire kan zolayar da ya yi masa a bara
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
