News
Shugaba Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Kai Ziyara Saudiyya Da Guinea Bissau
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaba Bola Tinubu ya dawo Abuja bayan wata ziyarar aiki ta kwanaki biyar da ya kai birnin Berlin na kasar Jamus, inda ya halarci taron G20 Compact.
Yayin da ya sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da misalin karfe 8 na daren Laraba, shugaban ya samu tarba daga manyan jami’an gwamnati da jam’iyyar APC mai mulki da suka hada da ministan babban birnin tarayya, Cif Nyesom Wike, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje, da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila.
A lokacin ziyarar, Shugaba Tinubu ya da hada kai da sauran shugabannin kasashe da gwamnatoci don bunkasa ci gaban tattalin arziki da kasuwanci a Afrika.
Taron na G20 shi ne karo na hudu, wanda gwamnatin Jamus da kungiyoyin ‘yan kasuwa suka shirya.
A ci gaba da karfafa alakar diflomasiyya, shugaban ya tattauna da shugaban gwamnatin Jamus, Olaf Scholz da wasu manyan jami’ai a ranar Litinin.
A wani labarin kuma Hatsarin Tirela Ya Yi Ajalin Mutum 25 A Jihar Neja
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
