Connect with us

News

Bangaren Shari’a Zai Iya Rasa Kimarsa A Idon ‘Yan Nijeriya -Bode George

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

Wani jigon jam’iyyar PDP, Cif Olabode George, ya yi Allah-wadai da matakin da alkalai suka dauka na soke nasarar zaben ‘yan siyasa.

George yana maida martani ne kan cece-kucen da kotun daukaka kara ta yanke a jihar Kano.

Advertisement

Ronaldo ya bukaci Alkalin wasa ya soke Fenality da ya bashi bayan ya gano akwai kuskure

Jaridar Inda Ranka ta ruwaito cewa kotun daukaka kara ta soke zaben gwamna Abba Yusuf na jihar Kano, yayin da ta bayyana Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar.

Amma rudani ya barke lokacin da Certified True Copy, CTC, na hukuncin ya nuna cewa kotun daukaka kara ta tabbatar da Yusuf a matsayin gwamnan Kano.

Advertisement

Amma Kotun Daukaka Kara ta danganta hakan da tuntuben alkalami da kuma rashin fahimta.

Da yake mayar da martani, George ya ce abin damuwa ne yadda ‘yan Najeriya suka daina amincewa da bangaren shari’a.

Advertisement

 

Da yake jawabi ga taron manema labarai a Legas a ranar Litinin, jigon na PDP ya ce,wannan tsarin yana da matukar damuwa domin idan mutane ba su yarda da bangare na uku na gwamnati ba, rikici ya kunno kai.

Advertisement

 

 

Advertisement

Tabbas, kawancen da ake yi tsakanin wasu ‘yan siyasa da alkalai yana da hadari ga dimokuradiyyar mu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending