Connect with us

News

Wata Sabuwa, Gwamnatin Ribas ta Fara Ruguje Ginin Majalisar Dokokin Jihar

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

Rikicin siyasar jihar Ribas ya dauki sabon salo a safiyar yau Laraba yayin da gwamnatin jihar ta fara rusa majalisar dokokin jihar.

Channels TV ta tattaro cewa kimanin Motocin rusau 10 ne suka shiga harabar majalisar a daidai lokacin da wasu ‘yan majalisar masu biyayya ga gwamnan jihar, Sim Fubara suka yi zaman farko.

Advertisement

Jirage Zasu Rika Biyan Diyya Ga Fasinjojin Da Suka Yi Jinkirin Tashi -Ministan sufurin jiragen sama

Zauren Majalisar ya samu halartar Masu biyayya ga Gwamnan Jihar Mai Ci wanda shugaban bangaren Edison Ehie ya jagoranta.

Jaridar Inda Ranka ta rawaito a ranar Talata cewa babbar kotun jihar Ribas ta bayar da wani tsohon umarni na amincewa da Edison Ehie a matsayin sahihin kakakin majalisar dokokin jihar Ribas.

Advertisement

Bangaren kakakin Majalisar, Ehie, a yayin zaman, ya bayyana cewa ginin ya kamata a gyara bayan fashewar da ta afku a ginin a ranar 30 ga watan Oktoba, 2023, yana mai cewa gwamnan zai samar musu da wani wurin da za su zauna kafin nan.

 

Advertisement

Idan dai ba a manta ba, Majiyar mu ta rawaito a ranar Litinin din da ta gabata cewa ‘yan majalisar dokokin jihar Ribas su 27 masu biyayya ga tsohon gwamna kuma ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, sun fice daga jam’iyyar PDP mai mulki, inda suka koma jam’iyyar adawa ta APC a jihar

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending