News
Ina sane da sadaukarwar da yan najeriya suke yi saboda sauye-sauyen gwamnati -Tinubu
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce yana sane da irin “sadaukarwar” da ‘yan ƙasar ke yi game da sauye-sauyen da gwamnatinsa take aiwatarwa tun bayan hawansa mulki a watan Mayu.
Cikin saƙon Kirsimeti da ya aika wa mabiya addinin Kirista, shugaban ya nemi ‘yan Najeriya su yi amfani da lokacin bikin da kuma hutu wajen “lura da ‘yan uwa saboda akwai waɗanda za su iya shiga cikin ƙunci, ko makoki, ko kuma waɗanda suka gaza cimma wani burinsu”.
Masu jiran a zartas masu da hukuncin kisa sun kai mutum 3,413 -Jami’in Kurkuku
Haka nan, ya bayyana 2023 a matsayin “shekarar sauyi a ƙasarmu”, yana mai cewa “ina sane cewa sauye-sauyen da suka zama tilas da muke aiwatarwa don samun ƙasa mai yalwa da arziki sun jawo sadaukarwa ta musamman”.
Ya ce: “Ina ƙarfafa muku gwiwa cewa nan gaɓa kaɗan, cikin jajircewarmu, za mu wayi gari cikin wata rana mai cike da zaman lafiya, da cigaba mai ɗorewa.”
Ya kuma nemi ‘yan Najeriya su yi amfani da damar wajen yi wa dakarun ƙasar maza da mata addu’a . “Allah ya kare su, ya mayar da su wajen iyalansu lafiya,” in ji shi.
Wannan ne bikin Kirsimeti na farko da shugaban zai yi a kan karagar mulki, wadda ta zo wa ‘yan Najeriya cikin ƙalubalen cire tallafin man fetur, da tsadar kayayyaki, da taɓarɓarewar matsalar tsaro.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
