News
Rundunar ’yan sandan Jihar Jigawa ta kama mutum 26 da ake zargi da aikata kwacen Waya
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Rundunar ’yan sandan Jihar Jigawa ta kama mutum 26 da ake zargi da aikata kwacen wayoyi da kuma shan muggan kwayoyi.
Kakakin rundunar, DSP Lawan Shiisu, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Dutse.
Ina sane da sadaukarwar da kuke yi saboda sauye-sauyen gwamnati -Tinubu
Ya ce kamen ya biyo bayan wasu jerin samame da suka kai a tsakanin ranar 18 zuwa 19 ga watan Disamba, a kananan hukumomi hudu na jihar.
Kakakin ya ce jami’an rundunar sun kama wani matashi kan zargin satar waya da kuma sata kudi Naira 10,000 a garin Babura da ke Karamar Hukumar Babura.
Aminiya ta ruwaito cewa sun kama wasu mutum biyu kan zargin laifin satar kwamfutoci shida da babur a Hadejia.
A wani labarin kuma Ina sane da sadaukarwar da kuke yi saboda sauye-sauyen gwamnati -Tinubu
Babban Bankin Najeriya CBN ya sauya matsayarsa kan hada-hada da kuɗin intanet ko kuma cryptocurrency a ƙasar.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito wata sanarwa da bankin ya fitar ranar Juma’a da ke umartar bankunan kasuwanci na Najeriya cewa su yi watsi da haramcin da ya saka kan amfani da kuɗin na crypto tu a 2021.
CBN ya ce yadda ake yayin kuɗin na crypto yanzu a faɗin duniya ya nuna irin buƙatar da ake da ita ta saka dokoki a kan sa.
“A watan Fabarairun 2021 CBN ya haramta wa bankuna da sauran cibiyoyin kuɗi amfani da cryptocurrency saboda almundahanar kuɗi da kuma ɗaukar nauyin ta’addanci,” in ji sanarwar.
“Sai dai kuma, abin da ke faruwa a duniya ya nuna cewa akwai buƙatar a kula da dukiyoyin hada-hada ta intanet wato Virtual Assets Service Providers (V/ASPs).”
Ya ƙara da cewa hukumar kula da hada-hada da hannayen jari za ta fitar dokoki da sharuɗɗan amfani da dukiyoyoin intanet ɗin.
Amma babban bankin ya jaddada haramcin yin kasuwanci, ko kuma mallakar asusun crypto ga bankunan kasuwancin su da kansu
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
