Connect with us

Sports

FIFA Ta Yi Barazanar Haramta Wa Kasar Brazil Da Kungiyoyinta Buga Duk Wata Gasar Kasa Da Kasa

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

Hukumar kula da kwallon kafa ta duniya, FIFA, ta yi barazanar dakatar da kungiyar kwallon kafa ta kasa da kungiyoyin kwallon kafa na kasar Brazil daga buga gasar kasa da kasa, idan har hukumar kwallon kafa ta kasar ta shiga tsakani wajen zaben sabon shugaban hukumar a watan Janairu.

FIFA ta bayyana hakan ne a cikin wata wasika da ta aike wa wani jami’in hukumar kwallon kafa ta Brazil (CBF) inda ta ce, hukumar na iya fuskantar dakatarwa idan ba ta yi biyayya ga kiran FIFA na jira ba, saboda hukumar na shirin bijerewa ta gudanar da zaben cikin gaggawa don maye gurbin Ednaldo Rodrigues a matsayin shugaban hukumar.

Advertisement

Hakkin tabbatar da zaman lafiya ya rataya a kan mu ne duka – Tinubu ga Gwamnoni

A cewar rahotannin ESPN da Kamfanin Dillancin Labarai na Associated Press, Kotun Rio de Janeiro ta kori Rodrigues da dukkan wadanda ya nada a hukumar CBF daga mukaminsu a ranar 7 ga watan Disamba saboda wasu kura-kurai da aka samu a zabensa na bara. Manyan kotunan Brazil biyu sun amince da hukuncin a makon jiya.

Hukuncin da aka yanke wa Rodrigues mai shekaru 69 na iya yin illa ga yunkurin Brazil na karbar bakuncin gasar cin kofin duniya ta mata a 2027 da kuma yunkurin da yake yi na daukar kocin Real Madrid, Carlo Ancelotti ya jagoranci tawagar kasar a shekara mai zuwa.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending