Connect with us

News

Kotu Ta Daure Masu Laifin Fyade Daurin Rai Da Rai A Jihar Jigawa

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

Advertisement

Wata Babbar kotun jihar Jigawa mai lamba 6 da ke zamanta a Birnin-Kudu ta samu wani matashi mai suna Habibu Haruna dan shekara 25 da haihuwa da laifin yi wa wata yarinya ‘yar shekara 14 fyade tare da yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

An gurfanar da wanda ake tuhuma a gaban babbar kotu da laifin janyo yarinyar zuwa dakin matarsa da ke Basirka a karamar hukumar Gwaram.

Advertisement

Za A Riƙa Yin Gwajin Hiv Kafin Aure A Jihar Kano

Alkalin kotun, Mai shari’a Musa Ubable, ya samu wanda ake tuhuma da laifi don haka ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

A lokacin da ake sauraren karar, kotun ta saurari shaidu biyar, sannan kuma lauyan masu gabatar da kara ya gabatar da shaidu uku don tabbatar da karar ba tare da wata shakka ba.

Advertisement

Kotun ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai a kan wanda aka samu da laifin daurin rai da rai bisa sashe na 3 karamin sashe na 2 da na 4 na dokar hana cin zarafin jama’a, dokokin jihar Jigawa mai lamba 2 na shekarar 2021.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending