Connect with us

News

Kotun Shari’ar Musulunci A Kano Ta Bada Umarnin A Duba Lafiyar Kwakwalwar Murja Kunya.

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Kotun shari’ar addinin muslinci ta Gama PRP Kano, karkashin jagorancin mai shari’a Nura Yusuf Ahmad, ta yi umarnin a binciki lafiyar kwakwalwar yar din nan Murja Ibrahim kunya.

Advertisement

Yar Tiktok: An Yanke Wa Ramlat Princess Hukuncin Zaman Gidan Yari na watanni 7

Gwamnatin Jihar Kano ‘Ba Za Ta Yi Katsalandan A Shari’ar Da Ake Yi Wa Murja Kunya Ba’

Cikin wani kwaryar kwaryar hukunci da kotun ta yi ta ayyana cewar a ajiye Maurja a karkashin kulawar likita kuma hukumar Hisba ta dinga lura da ita.

Advertisement

 

Mai shari’a Nura Yusuf ya bayyana cewar kasancewar ita murja ta nuna wani hali wanda yake nuna cewar ko dai tana cikin maye ko kuma kwakwalwarta bata da lafiya, a dan haka ne kotun ta yi umarnin ma’aikatar lafiya ta binkici kwakwalwar ta.

Advertisement

 

An kuma ayyana cewar zata kwashe watanni uku a karkashin kulawar likitoci da hukumar Hisba.

Advertisement

 

A karshe kotun ta yi addu’ar Allah ya shirya mana zuri’a.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending