Connect with us

News

Kira da data sun dawo daidai bayan katsewar wayoyin teku – HukumarNCC

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Hukumar Sadarwa ta Ƙasa, NCC, ta ce an dawo da sabis din kira da na data bayan katsewar da wayoyin sadarwa su ka yi a ƙarƙashin teku.

Advertisement

Daraktan Hulda da Jama’a na Hukumar NCC, Dr Reuben Muoka, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Litinin a Abuja.

Yan sanda sun kama matar da ta hada baki da saurayinta ayi garkuwa da ita don ‘yan uwanta su biya  kudin fansa

Mista Muoka ya ce an maido da sabis din ne, biyo bayan katsewar da wayoyi su kayi a Teku a Cote de’Ivoire da Senegal a ranar 14 ga watan Maris, wanda ya haifar da matsalar kira da data.

Advertisement

“Muna farin cikin sanar da cewa a yanzu an maido da sabis zuwa kusan kashi 90 cikin 100 na mafi girman karfin amfani da su,” in ji shi.

Muoka ya ce dukkan kamfanonin sadarwa da matsalar ta shafa sun dauki gabaran gyara ta hanyar gyaran na karkashin ruwa ta hanyar amfani da wadanda basu katse ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending