Connect with us

News

Ƴadda wani magidanci ya kashe matarsa kan ta dauki wayarsa

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA 

Rundunar yan sanda a jihar Adamawa ta ce ta kama wani mahauci mai shekara 33, mai suna Ibrahim Abubakar, mazaunin karamar hukumar Girei, da zargin kashe matarsa yar shekara 25, mai suna Hajara Sa’adu.

Advertisement

Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar, SP Suleiman Yahya Nguroje ya tabbatar wa da BBC faruwar lamarin, inda ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Kotu Ta Sa Ranar Gurfanar Da Ganduje Da Matarsa 

Nguroje ya ce bayan samun korafi daga wajen mahaifin marigayiyar ce kan abin da ya faru, nan take suka kama mijin nata.

Advertisement

Nguroje ya ce wanda ake zargin ya tabbatar da aikata laifin da ake zarginsa da shi, kuma ya ce ya kashe matar tasa ne bayan daukar wayarsa da ta yi.

“An same ta kwance cikin jini, sai aka tafi da ita zuwa asibiti inda likitoci suka tabbatar da rasuwarta,” in ji Nguroje.

Advertisement

Ya kara da cewa suna ci gaba da gudanar da bincike da kuma tattara hujjoji, kafin gurfanar da shi gaban kotu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending