News
DA DUMI-DUMI: Jaridar Inda Ranka ta taya al’ummar musulmi murnar Bikin Karamar Sallah
DAGÀ MARYAM BASHIR MUSA
A saƙon barka da Sallah da Jaridar ta aikewa musulman Najeriya da na Duniya gaba ɗaya, fatan Allah Ya karɓi ibadun da aka gudanar ya ba da lada.
Haka zalika ta ƙara kira na musamman ga al’ummar ƙasar da a haɗa kai waje guda a yi aiki tuƙuru domin a gina ƙasar.
“Najeriya ƙasa ce da za mu iya gina ta tayadda duk muke fata”. Inji jaridar Inda Ranka.
Jaridar ta kuma yi fatan al’umma za su rungumi abubuwan nagari da suka koya a cikin watan Ramadan su cigaba da ɗabbaƙa su a kowane lokaci. Tare da fatan za a yi shagulgulan Sallah lafiya.
Advertisements
