News
Jaridar Inda Ranka Ta Taya Babban Editanta Yasir Sani Abdullahi Murnar Cika Shekaru 26 da Haihuwa
Kamfanin Yakam Multimedia, masu wallafa Jaridar Inda Ranka, ya taya babban editanta, Malam Yasir Sani Abdullahi, murnar cika shekaru 26 da haihuwa.
Sanarwar taya murnar na kunshe ne a cikin wata takarda da shugaban kamfanin, Kabiru Basiru Fulatan, ya sanyawa hannu a ranar Asabar, inda ya bayyana jin dadinsa kan irin gudunmawar da Yasir ke bayarwa tun daga shigarsa cikin gidan jaridar a matsayin mataimaki na musamman, har zuwa yadda ya kai ga zama babban edita.
A cewar Fulatan, “Yasir Sani Abdullahi ya kasance kwararren dan jarida mai kishin aiki da jajircewa. Muna alfahari da irin ci gaban da ya samu a cikin kankanin lokaci a fagen aikin jarida.”
Shugaban kamfanin ya kara da cewa suna fatan Allah ya kara wa Yasir shekaru masu albarka, cike da lafiya da kuma nasara a dukkan al’amuransa, musamman ma a fannin aikin jarida da ya ke gudanarwa da kishin kasa da kwazo.
