News
Sarkin Kano na 16 ya taya Al, ummar musulmi murnar shiga sabuwar shekarar musulunci
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammad Sanusi II, yana farin cikin mika sakon taya murna ga daukacin al’ummar Kano dangane da samun nasarar kammala shekarar Musulunci ta 1445 da kuma shiga shekarar 1446 ta hijirar annabi muhammad (S A W)
Sarkin Ya Kuma ya taya zababben gwamna Jahar Kano alhaji abba Kabir Yusuf murna shigowar sabuwar shekara ta hijiriyya tare dayin addu,ar fatan zaman lafiya da kwanciyar hankalin da dukkan Al,ummar musulmin duniya
Sannan ya yabawa shugaban kasa, Nigeria Asiwaju Ahmed Bola Tinubu da Sarkin musulmin alhaji Sultan Abubakar Sa’ad wadanda yace sun sadaukar da kansu wajen ganin an samar da zaman lafiya da hadin kai da ci gaban al’ummar Musulmi Nijeriya baki daya
Sarki sunusi na biyu II yayi kira ga shuwagabanni na a kawo karshen rikice-rikice a tsakanin Musulmi da kuma yin amfani da bambancin ra’ayi na Nijeriya domin ci gaban dukkan ‘yan kasa a cikin shekara mai zuwa da kuma gaba.
Daga karshe kuma ya gargadi al’umma da su tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a lokacin bukukuwan sabuwar shekara ta Musulunci.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
