Connect with us

News

NDLEA Ta Kama Sarkin Gargajiya Da Kuma Wani Mai Hidimar Kasa Da Fataucin Kwayoyi A Kano

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa, NDLEA, ta  kama wani matashi mai suna Yusuf Abdulrahman, mai shekaru 25, mai hidimar kasa, a karamar hukumar Sumaila ta jihar Kano, dauke da Loud mai nauyin kilo giram 1.250.

Advertisement

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Femi Babafemi, Daraktan yada labarai na  Hukumar NDLEA, ya fitar ranar Lahadi.

Shin Da Gaske Ne Ahmad Musa Ya Fice Daga Tawagar ‘Yan Wasan Nijeriya  

A halin da ake ciki, sanarwar ta ce a jihar Osun, an kama shugaban al’ummar Akarabata a Ile-Ife, Ba’ale Ige Babatunde, mai shekaru 50, a ranar Juma’a 5 ga watan Yuli da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 5.

Advertisement

Yayin da yake yabawa jami’ai da jami’an runduna ta musamman da ke Osun, Benue, Ondo, Kano, da kuma babban birnin tarayya Abuja bisa kamawa, Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (Rtd) ya lura da kokarin da suke yi na rage samar da magunguna daidai da ayyukan wayar da kan jama’a na WADA yayin da ya umarei su da ‘yan uwansu a duk fadin kasar nan da su kula da lokaci.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending