Connect with us

News

Jam’iyyar PDP ta lashe zabukan kananan hukumomin Jihar Adamawa

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Kamar yadda sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar ta fitar yanzu haka, jam’iyyar PDP mai mulkin jihar ta lashe dukkan kujerun kansiloli a mazabu 226 dake jihar, in ban da gundumar Demsa dake karamar hukumar Demsa inda jam’iyyar NNPP ta lashe kujerar kansila daya.

Advertisement

 

Shugaban hukumar zaben na Jahar Mohammed Umar, ya ce jam’iyya mai mulki ta samu gagarumar nasara a dukkanin kananan hukumomin jihar 21, ya bayyana sakamakon ne a yammacin Lahadi a hedikwatar hukumar da ke Yola, babban birnin jihar.

Advertisement

 

Umar ya ce daga cikin jam’iyyun siyasa 19 da suka yi wa rajista a jihar, 12 ne suka shiga wannan atisayen.

Advertisement

 

Zaben kananan hukumomin jihar Adamawa shi ne na farko bayan da kotun koli ta bai wa mataki na uku ‘yancin cin gashin kai na harkokin kudi, inda ta umurci gwamnatin tarayya da ta biya kashi 20.60% na kason kudaden kananan hukumomi 774 na kasar nan kai tsaye zuwa asusunsu na kebantattu, ba wai ga asusun ajiyar su ba. ta gwamnatin jahohi ba

Advertisement

 

Kotun kolin da ta yanke hukunci a ranar Alhamis din da ta gabata ta kuma haramtawa gwamnoni masu shaye-shayen madafun iko rusa kananan hukumomin da aka zaba ta hanyar dimokuradiyya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending