Connect with us

News

Stallion Times Ta Shirya Taron Tattaunawa Akan Shugabanci Na Gari A Kano

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Shugaban Kamfanin Stallion Times Media Services, Isiyaku Ahmed, ya bayyana cewa shugabanci nagari ya kunshi hada kai da gwamnati da kungiyoyin fararen hula domin tabbatar da gaskiya da rikon amana.

Tattaunawar da ta kunshi kafafen yada labarai, kungiyoyin farar hula, gwamnati, da kuma kamfanoni masu zaman kansu na jihar Kano.

Gwamnan Sakkwato Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Da Ta Kwace Wa Sarkin Musulmi Ikon Nada Hakimai Da Dagattai.

Jaridar INDA RANKA ta ruwaito cewa an gudanar da taron ne a cibiyar ‘yan jarida da ke Kano a ranar Alhamis.

Ahmed ya lura da cewa yan Najeriya na fama da matsananciyar rashin aminta da gwamnati wajen aiwatar da manufofin da ke nuna muradin ‘yan kasa.

“Kyakkyawan shugabanci shi ne tsarin da ake sarrafa yan kasa da gudanar da ayyukanta, da kuma tsarin da ita da al’ummarta ke bi da su,” inji shi.

Advertisement

 

Makasudin tattaunawar da aka yi a kan shugabanci na gari, wanda gidauniyar MacArthur ta tallafa, shi ne wayar da kan masu gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu don inganta samar da ababen more rayuwa da muhimman ayyuka ga ‘yan kasa.

Tattaunawar ta zagayowar ta mayar da hankali ne kan inganta karfin masu ruwa da tsaki kan tsare-tsare da dabarun yin aiki mai inganci tare da kamfanoni masu zaman kansu, don karfafa gwiwar ‘yan kasa da su shiga harkokin mulki da inganta ayyukan more Rayuwa

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending