Connect with us

News

Sanata Ndume Ya Ki Amincewa Da Sabon Ofishin Da Aka Bashi A Majalisar Dattawa

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Sanata mai wakiltar Borno ta kudu a majalisar dattawan Nijeriya, Mohammed Ali Ndume, ya yi watsi da sabon ofishin da kwamitin ayyuka na majalisar dattawa ya bashi.

Advertisement

Ndume, a wata wasika da ya aike wa shugaban kwamitin ayyuka na majalisar dattawa a ranar Talatar nan, ya ce ofishin da aka ba shi bai nuna girmansa da matsayinsa a majalisar dattawa ba.

Zanga-Zanga: Gwamnatin  Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun

Wasikar mai dauke da sa hannun babban sakataren sa,Yati Shuaibu Gawu, ta ce: “An umurce ni da in sanar da ku cewa, Sanata Mohammed Ali Ndume, ya ki amincewa da ofishin da aka bashi mai lamba 3.10 da kwamitin ayyuka ya yi.

Advertisement

Jaridar INDA RANKA ta ruwaito kwanakin baya ne aka tube Ndume daga mukaminsa na babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, biyo bayan sukar da ya yi wa gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending