News
Gobara Ta Ƙone Rijiyar Kamfanin Man NNPCL
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar kula da tace man fetur ta NUPRC, ta ce sun samu rahoton kamawar gobara a rijiyar Akaso mai baki huɗu da kamfanin NNPC ke gudanarwa a ranar Asabar.
Wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Laide Shonola ya fitar a ranar 3 ga watan Agusta ta ce, lamarin ya auku ne da misalin ƙarfe 11:12 na dare a ranar Juma’a inda gobarar ta faɗaɗa zuwa rafin da ke kusa da wajen.
Shiyyar gudanarwa ta 18 ta NNPC ta tabbatar da cewa an samu ɗaukin gaggawa domin kashe gobarar da kuma keɓance wajen ta hanyar amfani da wasu sinadarai da ke hana bazuwarta zuwa wasu wurare.
Haka nan, sanarwar ta ce su na ƙoƙarin maye gurbin man da aka rasa inda tuni su ka aika jirgin ruwan kamfanin da kuma jami’an sanya ido domin kulao da yanayin wajen.
Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa Kawo yanzu dai, ba a gano dalilin aukuwar lamarin ba wanda a halin yanzu ta naɗa kwamitin bincike da ya ƙunshi masu-ruwa-da-tsaki domin gano musabbabin aukuwar lamarin.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
