Connect with us

News

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero Ya Kai Ziyarar Jaje Kasuwar Kwari

Published

on

IMG 20241006 WA0184.jpg

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero  ya kai ziyarar jajantawa Yan kasuwar Kantin Jim kadan da dawowarsa daga ziyarar aiki da yaje Abuja.

Advertisement

Dubun dubatar Masoya da magoya baya ne sukayi cincirundo domin raka mai Martaba Sarkin kasuwar ta Kantin kwari.

Akwai Yuwuwar NNPC Ya Sake Fitar Da Farashin Man Fetur A Najeriya

Da yake jajantawa wadanda suka gamu da ibtila’in gobarar, Sakin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yayi addu’ar Allah ya mayar da asarar da akayi a kasuwar tareda addu’ar Allah ya kiyaye afkuwar hakan anan gaba.

Advertisement

Alhaji Aminu Ado Bayero ya kuma godewa Jami’an Hukumar kashe gobara ta jihar Kano da Jami’an tsaro da Kungiyar Yan kasuwar da dai daikun al’uma bisa yadda suka bada dugunmawa wajan tabbatar da kashe gobarar.

Sarkin daga nan sai ya bukaci Yan kasuwa da sauran al’uma su cigaba dayin addu’oi domin kiyayewar afkuwar irin wannan ibtila’i tareda neman samun sassaucin al’amura na rayuwar yau da kullum.

Advertisement

Mai Martaba Sarkin na Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yakai ziyarar aiki ne babban Birnin Tarayya Abuja tareda halartar wasu tarurruka, inda daga dawowar sa ne ya zarce domin yin jaje ga Yan kasuwar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending