Connect with us

Opinion

Muhimmin Sako Zuwa Ga Gwamnonin Jihohin Arewa, Da Manyan Arewa Baki Daya!!!

Published

on

images
Spread the love

 

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

 

Advertisement

Assalamu alaikum

 

Ya ku masu girma manyan mu da shugabannin mu na arewa, ya kamata ku sani, yanzu haka jihar Legas ita kadai, tayi shiri na musamman domin samar da wutar lantarki har megawatts dubu hudu (4,000mgw), kusan abinda kasar Najeriya ta ke da shi kenan, kuma har wannan shiri yayi nisa sosai. Kuma ku sani, wallahi yin hakan zai zama sanadiyyar janye masana’antu da harajin kasar baki daya zuwa birnin Legas.

Advertisement

 

Ina aiko da wannan sako ne zuwa ga re ku domin ku kara farkawa, ku fadaka, domin kuma ku fara tunanin nemo wa arewa mafita in dai har da gaske kuke yi.

 

Advertisement

Wannan sauke hakki ne da Allah Subhanahu wa Ta’ala ya dora muna mu sanar da ku. Idan kuma kun yi watsi da shi, to Allah shaida ne akan cewa mun sanar da ku.

 

Allah yasa mu dace, Allah ya baku ikon duba wannan sako da idon basirah, amin.

Advertisement

 

Nagode,

 

Advertisement

Wassalamu alaikum,

 

Dan uwanku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. 08038289761.

Advertisement

 

Laraba, 27/11/2024.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *