News
Buhari Ya Magantu Game Da Labarin Da Ake Yadawa Cewa An Kwace Filin Sa A Abuja.
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Malam Garba Shehu, mai magana da yawun tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya magantu game da labarin da ake yadawa cewa an kwace filin mai gidansa a Abuja.
A wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, Garba Shehu, ya ce Buhari ba shi ne mai wannan filin da ake magana ba, an bayar da shi ga gidauniyar Muhammadu Buhari.
A baya-bayan nan ne wasu sunaye sama da 700 suka fita cewa ministan Abuja ya kwace takardun filayen ciki har da tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
