Connect with us

Politics

Abbas Sani Abbas Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP Zuwa APC 

Published

on

FB IMG 1736591113320
Spread the love

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

 

Advertisement

 

 

Tsohon Kwamishinan Raya Karkara da Cigaban Al’umma na Jihar Kano, Abbas Sani Abbas ya fice daga jam’iyyar (NNPP) zuwa Babbar jam’iyya mai Mulki ta  (APC).

Advertisement

 

Abbas wanda yana daya daga cikin kwamishinoni shida da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sauke daga mukamansu a watan da ya gabata, ya bayyana sauya shekarsa a wata ziyarar da ya kai’wa wasu jiga-jigan jam’iyyar APC a Kano.

 

Advertisement

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin ne ya karbeshi tare , da tabbatar da matakin Hon Abbas a matsayin tuna ni mai Kyau kamar Yadda  ya wallafa a shafinsa na  Facebook a ranar Laraba.

 

 

Advertisement

 

Jibrin ya yabawa Abbas bisa jajircewarsa na hada kai da jama’iyyar tasu  tare da nuna kwarin guiwa kan yadda zai bayar da gudunmawar ci gaban jam’iyyar.

 

Advertisement

Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Kano Abdullahi Abbas, da sauran shugabanni, sun rungumi Abbas Sani Abbas hannu Biyu Biyu tare da bashi tabbacin goyon baya kuma zamu hada kai don samar da makoma mai kyau ga jihar Kano da ma Najeriya Baki daya..

 

Ana kallon ficewar Abbas a matsayin wani gagarumin ci gaba a fagen siyasar Kano yayin da jam’iyyar APC ke ci gaba da karfafa matsayinta a jihar.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *