News
SERAP Ta Maka Shugaba Tinubu Da Gwamnoni A Kotun ECOWAS Bisa Zargin Tauye Hakkunan ‘Yan Nageriya
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kungiyar dake fafutukar wajen Kare cin hanci da rashawa ta Kasa da Ƙasa a Nageriya (SERAP) ta maka Shugaba Tinubu da Gwamnoninsa a kotun ECOWAS kan zalunci da hana yan Ƙasa damar tofa albarkacin bakinsu a shafukan sada zumunta.
A cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a ranar Lahadi, SERAP ta ce ‘Yan Ƙasa nayin amfani da shafukan sada zumunta ne domin bayyana irin abubuwan da akeyi musu amman gwamnatin Bola Tinubu take take hakkunan ‘yan Najeriya na fadin albarkacin bakinsu, tare da tauye hakkunanasu na bayyana irin dabi’un da gwamnati ke aikatamusu.
SERAP ta ce, “Muna nemi kotun ECOWAS ta dakatar da gwamnatin Tinubu da gwamnonin Ƙasar su 36 yin amfani da dokar ta’addanci a shafukan sada zumunta ta 2024 don hukunta halastattun maganganu da kuma hukunta ’yan Najeriya ciki har da masu amfani da shafukan sada zumunta.
“Maimakon yin amfani da dokar da aka yi wa kwaskwarima don tabbatar da tsaro ta shafukan sada zumunta da masu amfani da ita, hukumomin Najeriya na ci gaba da sanya mata makami don dakile ‘yancin dan Adam da ‘yancin ‘zarafin yan jarida,” in ji kungiyar.
Karar da SERAP, ta shigar mai lamba ECW/CCJ/APP/03/2025 a makon da ya gabata a gaban kotu a Abuja kungiyar ta nemi Kotun data hana gwamnatin Bola Tinubu da Gwamnoninsa take hakkin Yan Nageriya.
Jaridar Peaple Gezette ta rawaito Wannan mataki na zuwa ne bayan kotu ta tsare wata ma’aikaciyar jinya kuma mai fafutuka, Olamide Thomas bisa zargin cin zarafi a shafukan sada zumunta kan kalaman Mista Tinubu, da dansa Seyi Tinubu, da kuma ‘ya’yan ‘yan sanda biyu.
An kuma kama wani fitaccen dan Tick tok mai suna Seaking bisa sukar Shugaba Tinubu da Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Egbetokun, a wani faifan bidiyo inda ya yi Allah wadai da kakakin ‘yan sandan, Muyiwa Adejobi, da ya ce hakan laifi ne. don cin mutuncin mutane akan layi.
