Connect with us

News

An Dakatar Da Sheikh Bin Uthman Daga Limancin Masallacin Sahaba, DSS Ta gayyace shi

Published

on

FB IMG 1738307264328

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Kwamitin kula da Masallacin Sahaba da ke Kano ya dakatar da fitaccen Malamin nan Sheikh Bin Uthman daga Limanci a Masallacin sakamakon zarginsa da rura wutar sabani game da jagorancin Masallacin.

Advertisement

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa, hukumar tsaro ta DSS ta gayyaci Shehin Malamin kan wannan batu, inda ta bukace-shi da karya gudanar da huduba ko furta wata kalma da za ta tunzura magoya baya su tada zaune tsaye.

Yan Sanda Sun Cafke Ango A Ranar Ɗaurin Aurensa 

Wata majiya ta shaidawa jaridar cewa, tun a washegarin faruwar hatsaniyar da ta faru a Masallacin ne hukumar kula da Masallacin ta tura wa Shehin Malamin da takardar dakatar wa, inda a ranar litinin kuma hukumar tsaron DSS da Council of Ulama suka zauna da Sheikh Bin Uthman, har ma bayanai sun ce Council of Ulama sun shawarci Sheikh Bin Uthman da ya hakura da wannan sabon Masallacin ya koma tsohon Masallacin sa na Sahaba domin ci gaba da Limanci acan.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending