Connect with us

News

Yan Sanda Sun Cafke Ango A Ranar Ɗaurin Aurensa 

Published

on

Yan sanda sun cafke wani ango a ranar ɗaurin aurensa kan zargin kisan kai

DAGA MAIMUNATU BASHIR MUSA 

‘Yan sanda sun kama wani mutum a ranar ɗaurin aurensa kan zargin kashe wani mutum bayan sun yi faɗa a jihar Neja.

Advertisement

Jamilu Saidu, mazaunin unguwar Kumbashi da ke ƙaramar hukumar Mariga da ake zargi da kashe Iliyasu Aminu mai shekaru 30.

Hasken Waya Da Na Computer Na Kawo Lahani Ga Idanu   —kwararren likitan ido

Jami’in rundunar ‘yan sandan jihar, Wasiu Abiodun, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar.

Advertisement

Ya ce an samu wani faɗa ne da ya ɓarke tsakanin ƙauyuka biyu na Yabawa da Ungwar Sarkin-Daji, a yayin wani biki a yankin Kumbashi.

Mai magana da yawan ‘yan sandan, ya ce, Saidu ne ya sari marigayi Aminu da wuƙa a ka wanda ya jawo mutuwarsa.

Advertisement

“A ranar 18 ga watan Janairun 2025 da misalin ƙarfe 8:00 na yamma ne ‘yan sanda dags Bangi suka kama Jamilu Saidu da ke unguwar Kumbashi a ƙaramar hukumar Mariga saboda zargin kisan kai.”

Mista Abiodun ya ce wanda ake zargin ya amsa laifinsa kuma tuni aka mai da shi sashen kula da manyan laifuka (SCID) da ke Minna domin cigaba da bincike don gurfanar da shi a gaban kotu.

Advertisement

 

 

Advertisement

PREMIUM TIMES

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending