Connect with us

News

Mazauna Rimin Zakara Sun Yi Zanga-Zanga Kan Rushe Musu Gidaje Da Kwangaye

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar Hukumar Ungoggo a Jihar Kano sun numa matukar damuwa da abin da ya faru a Unguwar ,inda aka zargi wasu jami’an tsaro tare da motocin rushe gurare da hallara a yankin, inda suka rushe gidaje da kwangaye.

Advertisement

Wannan mataki ya janyo bacin rai daga mazauna yankin, lamarin da ya haddasa tashin hankali har ya kai ga kone gidan mai gari, wanda al’ummar unguwar suka zarga da hannu a lamarin.

Ahmed Garba Yaro Yaro Ya Zama Sabon Mai Horar da Kano Pillars

Rahotanni sun nuna cewa an harbi mutane shida yayin rikicin, sannan an yi jana’izar mutane biyu. Wannan lamari ya tayar da hankalin al’umma, kuma har yanzu ba a samu cikakken bayani daga rundunar ‘yan sandan Jihar Kano kan batun ba.

Advertisement

EXPRESS RADIO ta ruwaito cewa Mazauna Unguwar  sun kira ga hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiya da tabbatar da adalci ga al’ummar yankin.

Haka kuma, Sun kira da a kwantar da hankula tare da bin doka da oda domin zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending