Connect with us

Sports

Ahmed Garba Yaro Yaro Ya Zama Sabon Mai Horar da Kano Pillars

Published

on

IMG 20250203 WA0007

DAGA MAIMUNA RABIU UMAR 

Kungiyar Kano Pillars ta sanar da nada tsohon dan wasan Super Eagles da Borussia Dortmund, Ahmed Garba Yaro Yaro, a matsayin sabon mai horar da kungiyar.

Advertisement

Wannan mataki ya biyo bayan dakatar da tsohon kocin kungiyar, Usman Abdullah, sakamakon rashin kyakkyawan sakamako da kungiyar ke samu a wannan kakar wasa.

Mawallafin Jaridar NIGERIAN TRACKER Ya Zama Ma’ajin Kudi na Kungiyar Northern Online Media Group

Rashin nasara da Pillars ta yi da ci 4-1 a hannun Ikorodu United, tare da canjaras da Bayelsa United, ya haifar da gagarumin ce-ce-ku-ce a tsakanin magoya baya da shugabannin kungiyar, wanda hakan ya kai ga matakin sauya mai horarwa.

Advertisement

A cewar shugaban kungiyar, Alhaji Ali Nayara, Yaro Yaro – wanda tsohon dan wasan Kano Pillars ne – zai jagoranci kungiyar na wucin-gadi har sai kwamitin da aka kafa domin binciken Usman Abdullah ya kammala aikinsa, kafin a dauki matakin gaba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending