Connect with us

News

Kano Pillars Ta Dakatar Da Kocinta Usman Abdullah Na Tsawon Makonni Uku

Published

on

FB IMG 1738525063435

DAGA UMAR ABDULLAHI HOTORO

 

Advertisement

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta dakatar da Kocinta Usman Abdalla, tsawon makonni uku, sakamakon rashin ƙoƙari da kuma nuna halayyar da bata kamata ba ga magoya bayan ƙungiyar.

Kungiyar ta ɗauki wannan matakin ne bayan tashi daga wasan da ta buga canjaras (0-0) da Bayelsa United a filin wasa na Sani Abacha a ranar Lahadi 2-02-2925.

Advertisement

 

Dakatarwar ta biyo bayan rashin tabuka abin a zo a gani a baya bayan nan, da kuma harzika magoya bayan kungiyar, bayan tashi daga wasan da Kano Pillars din ta buga chanjaras da Bayelsa United a filin wasa ana Sani Abacha dake Kano.

Advertisement

 

Ƙungiyar dai tana fama da rashin nasara a ƴan kwanakin nan inda a cikin wasanni uku wasa ɗaya kawai ta samu nasara a kai.

Advertisement

Bayan tashi daga wasan ne magoya bayan ƙungiyar suka yi wa Usman Abdalla ihu, kamar yadda rahotanni suka bayyana, lamarin da bai yi wa mai koyarwar daɗi ba shi kuma ya mayar da martani.

Cikin wata Sanarwar da Shugaban hukumar gudanarwar kungiyar Alhaji Ali na Yara Maisamba ya sanyawa hannu ta ce, mataimakin mai horaswar Tsohon ɗan wasan ƙungiyar, Ahmad Garba Yaro-Yaro, shi ne zai ci gaba da jagoranci ƙungiyar a matsayin riƙon ƙwarya tare da taimakon Abubakar Musa da tsohon ɗan wasa Gambo Muhammad da Sulaiman Shua’aibu da kuma Ayuba Musa

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending