Connect with us

Sports

SWAN Ta Karrama Ahmad Hamisu Gwale A Matsayin Gwarzon Mai Gabatar Da Shirin Wasanni A Kano

Published

on

IMG 20250207 WA0003

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Kungiyar Ƴan jaridu marubuta labaran wasanni ta ƙasa reshen jihar Kano ta karrama Ahmad Hamisu Gwale na Premier Radio Kano a matsayin gwarzon mai gabatar da labarin wasanni na shekarar 2024.

Advertisement

Kungiyar ta karrama ɗanjaridar ne yayin taron ƙaddamar da kalandar kungiyar ta shekerar 2025, da ya gudana a sakateriyar yan jaridu ta jihar Kano yau Alhamis.

Yan Bindiga Sun Sace Tsohon Shugaban NYSC da Wasu Mutane 

Ahmad Hamisu Gwale dai ƙwararren ɗanjarida ne da ya ƙware wajen gabatar da shirye-shiryen wasanni kuma yana ɗaya daga cikin Masu gabatar da shirin ZAUREN WASANNI na tashar Premier Radio Kano Haka zalika shine mai magana da yawun kungiyar kwallon kafa ta BARAU FC.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending