News
Tinubu Ya Bukaci Gwamnan Kano Ya Warware Rikicin Jami’ar Bayero Da Al’ummar Rimin Zakara
DAGA KABIR BASIRU FULATAN
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bukaci gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da ya warware rikicin dake tsakanin Jami’ar Bayero ,Kano da kuma al’ummomin Rimin Zakara.
Tinubu ya yi rokonne a ranar Asabar yayin bikin karrama mutane 39 da Jami’ar Bayero ta gabatar wacce karamar Ministar Ilimi , Farfesa Suwaibhu Ahmed ta wakilta.
Jaridar Punch ta rawaito shugaban ya bukaci gwamna Abba Kabir ya dauki matakin gaggawa ta hanyar da ta da’ce domin warware matsalar Jami’ar da Al’umma gaba daya.
Baya ga haka Tinubu ya amince da zagaye sabbin rukunin Katangar jami’ar idan komai ya daidaita.
Haka zalika Shugaba Tinubu ya sake tabbatar da kudurin gwamnatinsa na inganta ayyukan samar da tallafi na al’umma a fading kasar.
Advertisements
