Connect with us

News

Jami’an Yan Sanda Sun Gano Gawar Almajiri da Aka Cire Masa Kai A Jigawa

Published

on

FB IMG 1741948974746

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da tsintar gawar wani almajiri dan shekara 14 mai suna Bashir Adamu, dalibin Malam Musa Wada, a kauyen Jikas-Dabaja da ke karamar hukumar Gwaram.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Shi’isu Lawan Adam, ya tabbatar da aukuwar wannan mummunar ta’asa, inda ya bayyana cewa an gano gawar yaron a gefen hanya bayan ya bata na tsawon kwanaki biyu.

Advertisement

Har yanzu ba a gano wanda ke da hannu a wannan aika-aika ba, amma hukumomi sun fara bincike don gano masu hannu a lamarin.

Cutar Sanƙarau Ta Kashe Sama Da Mutum 50 Yayin Da Cutar Ta Kama Sama Da Mutum 200 A Arewacin Najeriya

Wannan kisan gilla ya jefa al’ummar yankin cikin firgici da fargaba, inda jama’a ke kira ga hukumomi da su gaggauta daukar matakan kare rayukan ‘ya’yansu.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

SAWABA FM

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending