Connect with us

News

Cutar Sanƙarau Ta Kashe Sama Da Mutum 50 Yayin Da Cutar Ta Kama Sama Da Mutum 200 A Arewacin Najeriya

Published

on

Annobar cutar sanƙarau na ci gaba da barazana ga rayukan jama’a a jihohin Sokoto da Kebbi, inda rahotanni ke nuna cewa fiye da mutum 50 sun rasa rayukansu, yayin da cutar ta kama sama da mutum 200.

A jihar Kebbi, ƙananan hukumomin Aliero, Jega, da Gwandu sun fi fuskantar barazanar cutar, musamman ma a Aliero, inda aka ce sai bayan da cutar ta yi ƙamari ne hukumomi suka farga. A Sokoto kuwa, Tambuwal ce ke fama da cutar, inda gwamnatin jihar ta ce tana ɗaukar matakan gaggawa.

Advertisement

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Ƙudurorin Sauya Dokar Haraji

Masana kiwon lafiya sun danganta yawaitar cutar da tsananin zafin da ake fama da shi a yankin. Yayin da hukumomi ke ƙoƙarin dakile yaduwar cutar, al’ummar yankin na cikin fargaba, suna bukatar taimakon gaggawa don hana yawaitar mace-mace.

 

Advertisement

 

FRI HAUSA 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending