Connect with us

News

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Ƙudurorin Sauya Dokar Haraji

Published

on

Majalisar wakilai ta ce gwamnonin na barazanar hana mambobinta takara a 2027 matukar suka goyi bayan dokar haraji ta Tinubu

 

Majalisar Wakilan Nijeriya ta amince da kudirin sake fasalin haraji da Shugaba Bola Tinubu ya miƙa wa majalisar dokokin kasar.

Advertisement

A ranar Alhamis ne Majalisar Wakilan ta amince da rahotan ƙudurorin gyara haraji guda hudu a zamanta da ta yi a Abuja, kamar yadda mai taimaka wa Shugaban Ƙasa na Musamman kan Watsa Labarai ya wallafa a shafinsa na X.

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari A Kauyuka Biyar A Kaduna

A yanzu ana jiran amincewar Majalisar Dattijai ne.

Advertisement

Kudurorin sun hada da dokar harajin Nijeriya da daftarin kula da haraji da dokar hukumar haraji, da kuma dokar kafa hukumar tattara kudaden shiga ta Nijeriya.

Wannan ya biyo bayan nazarin saɗara-saɗara na duk gyare-gyaren da suka dace akan kudurorin a Kwamitin Gabaɗaya.

Advertisement

Wasu daga cikin gyare-gyaren sun haɗa da barin harajin VAT a kan yadda yake a yanzu wato kashi 7.5 cikin 100, sabanin yadda aka so ƙara shi, da kuma tsawaita keɓance harajin kuɗin shiga ga takamaiman kasuwancin noma da jami’an soja.

Tare da amincewa da rahoton kan kudurorin haraji, Majalisar Wakilai na kokarin ganin ta amince da kudirin haraji a mako mai zuwa yadda zai zama doka.

Advertisement

Tsarin raba kuɗaɗen haraji na VAT da majalisar ta amince da shi:

Za a dinga raba kashi 50 cikin 100 daidai wa daida ga jihohin ƙasar

Advertisement

Sai kuma a raba kashi 20 cikin 100 bisa ga yawan jama’ar jihohi

Kashi 30 cikin 100 kuma za a raba shi bisa ga abin da yawan abin da jihohin ke samarwa

Advertisement

Kawar da damuwowin ‘yan Nijeriya

Da yake jawabi bayan majalisar ta yi nazari tare da amincewa da rahotan kudirorin gyara haraji guda hudu, Shugaban Kwamitin Kudi na Majalisar Wakilai, James Faleke, ya bayyana cewa an kawar da dukkan damuwar da ‘yan Nijeriya suka nuna a cikin takardun.

Advertisement

Dan majalisar ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa dokar sake fasalin haraji za ta samar da dokokin da za su samu karbuwa sosai.

“An shafe kwanaki uku ana zaman sauraron ra’ayoyin jama’a a kan waɗannan ƙudurorin, tare da gabatar da bayanai daga manyan masu ruwa da tsaki sama da 80. Bayan haka, mun gudanar da ganawa ta kwanaki takwas don yin muhawara a kan kowace saɗara.

Advertisement

“Na yi farin ciki da cewa ‘yan majalisar sun amince da kyakkyawan aikinmu kuma sun amince da duk shawarwarinmu,” in ji Faleke.

Majalisar ta yi gyaran fuska ga batun harajin gado mai cike da cece-kuce, inda ta bayyana cewa duk wani gadon da aka samu kafin rushe batun ba za a iya biya masa haraji ba.

Advertisement

Majalisar ta kuma amince da samar da ci gaba da ba da tallafi ga hukumomin TETFUND, NASENI, da NITDA ta hanyar asusun ci gaba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending