Connect with us

News

Gwamnatin Kano Ta Yi Allah-wadai da Rashin Bayyana Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara Kan Rikicin Masarauta

Published

on

1742052862999

 

Gwamnatin Jihar Kano ta nuna damuwa kan rashin bayyana hukuncin da kotun ɗaukaka ƙara ta yanke dangane da rikicin masarautar Kano.

Advertisement

A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, gwamnati ta umarci lauyoyinta da su yi nazarin umarnin kotun da aka bayar a ranar Juma’a, tare da ɗaukar matakin da ya dace da doka.

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Watsi Da Bukatar Kafa Sabbin Jami’o’i 200

Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano, Barista Haruna Dederi, ya bayyana cewa hukuncin kotun ɗaukaka ƙara na ranar 10 ga watan Janairu ya tabbatar da soke dokar masarautun Kano ta 2019, tare da soke hukuncin babbar kotun tarayya da ke Kano.

Advertisement

“Da Alhaji Aminu Babba Ɗan’agundi ya ga bai gamsu da hukuncin ba, sai ya garzaya zuwa kotun ƙoli,” in ji Dederi. Ya kuma jaddada cewa hukuncin kotun ɗaukaka ƙara na farko yana nan daram, har sai kotun ƙoli ta yanke nata hukuncin.

Gwamnatin Kano ta bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da ci gaba da gudanar da harkokinsu cikin lumana, yayin da take godiya ga ‘yan jihar bisa haƙurinsu da addu’o’in da suke yi domin zaman lafiya a jihar da ƙasa baki ɗaya.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending