News
Kanawa Sun Shiga Ruɗani: Waye Galadiman Kano na Gaskiya?
Yau Juma’a birnin Kano ya shiga cikin ruɗani bayan da sarakunan da ke ikirarin zama Sarakunan Kano biyu suka naɗa Galadima biyu dabam-dabam, lamarin da ya bar al’umma cikin tambaya kan wanene Galadiman Kano na gaskiya.
Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya naɗa ɗan uwansa, Sunusi Ado Bayero, a matsayin sabon Galadiman Kano, yayin wata walima da aka gudanar a fadar masarautar Kano da ke Nasarawa.
Dakarun Soji Sun Kashe Wasu Fitattun Shugabannin ‘Yan Bindiga Guda Uku A Zamfara
A lokaci guda kuwa, Sarkin Kano Muhammadu Sunusi II, ya naɗa ɗan uwan mahaifinsa, Munir Sunusi, a matsayin Galadiman Kano a wani biki da ya gudana a fadar Kofar Kudu, wanda Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya halarta.
Wannan sabani ya biyo bayan rasuwar marigayi Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sunusi, wanda ya bar gurbin da yanzu bangarori biyu ke takara akansa.
Masu sharhi na ganin cewa wannan naɗe-naɗen biyu zai iya jefa masarautar Kano cikin wani sabon rikici, musamman ganin yadda al’umma suka rabu kashi biyu – wasu na tare da Aminu Ado Bayero, yayin da wasu ke goyon bayan Muhammadu Sunusi II.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
