Connect with us

News

Buratai Ya Karyata Rahoton Harin Boko Haram

Published

on

FB IMG 1749458977984

Tsohon Babban Hafsan Sojin Najeriya kuma tsohon Jakadan Najeriya a Jamhuriyar Benin, Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai (rtd), ya karyata rahotannin da ke yaduwa a kafafen sada zumunta na cewa ‘yan Boko Haram sun kai masa hari a lokacin bukukuwan Sallah.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da makusancinsa, kuma tsohon Kakakin Rundunar Sojin Najeriya, Birgediya Janar SK Usman (rtd), ya fitar a ranar Litinin, 9 ga Yuni, 2025.

Advertisement

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 11 Da ‘Yan Bindiga Su Kai Ƙoƙarin Garkuwa Da Su

A cewarsa, labarin da ke yawo a dandalan sada zumunta kan wani hari da aka ce an kai wa Buratai, karya ce tsagwaronta, domin kuwa babu irin hakan da ta faru.

“Janar Buratai yana Abuja, inda ya gudanar da bukukuwan Sallah cikin kwanciyar hankali tare da iyalansa da abokansa, ba tare da wani abu makamancin hari ko barazana ba,” in ji sanarwar.

Advertisement

Sanarwar ta kara da cewa yaɗa irin waɗannan jita-jita marasa tushe da makama, alama ce ta rashin kishin ƙasa, da kuma yunƙurin tayar da zaune tsaye a tsakanin al’umma.

“Wannan nau’in jita-jita da aka saba gani daga wasu marasa kishin kasa ne, wadanda ke ƙoƙarin bata suna da tayar da hankalin jama’a ta hanyar yaɗa ƙaryar da ba ta da wata alaka da gaskiya,” in ji SK Usman.

Advertisement

Ya shawarci jama’a da su rika tantance sahihancin duk wani bayani da suke samu, musamman a kafafen sada zumunta, kafin yada shi, domin kauce wa ɗora al’umma kan hanyar rudani da tashin hankali.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending