Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Gargaɗi Kan Yiwuwar Ambaliya A Kano Da Sauran Jihohi 10

Published

on

Mutum 259 ne suka mutu yayin da 625,239 suka rasa matsugunansu a ambaliyar ruwa a Nijeriya – NEMA

Gwamnatin Tarayya ta fitar da gargaɗi kan yiwuwar ambaliya a Jihar Kano da wasu jihohi goma a faɗin ƙasar nan, daga ranar 16 zuwa 20 ga Yuli, 2025.

Wannan na cikin wata sanarwa da Cibiyar Fargabar Ambaliya ta Ƙasa (National Flood Early Warning Centre) ƙarƙashin Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya ta fitar ranar Laraba.

Advertisement

An Kama Dalibai 11 Da Ake Zargi Kan Kisan Dalibai Biyu A Makarantar Gwamnati A Kano

Jihohin da aka ambata a cikin rahoton sun haɗa da Adamawa, Akwa Ibom, Bauchi, Borno, Cross River, Jigawa, Kano, Katsina, Plateau, Yobe da Zamfara.

A Kano, rahoton ya bayyana cewa ana sa ran za a samu ruwan sama mai yawa a yankunan Kunchi, Birnin Kano, Gezawa, Wudil, Bebeji, Sumaila da Tudun Wada – lamarin da ka iya janyo ambaliya da illa ga rayuka da dukiyoyi.

Advertisement

Daraktan Sashen Kula da Lalacewar Ƙasa, Ambaliya da Gabar Teku a Ma’aikatar Muhalli, Usman Abdullahi Bokani, ya ce hukumomin da abin ya shafa a jihohin da aka ambata su gaggauta ɗaukar matakan kariya.

Ya kuma bukaci al’umma da su kasance cikin shiri da kuma bin shawarwarin da hukumomi za su bayar domin rage haɗarin ambaliya.

Advertisement

 

STALLION TIMES 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending