Connect with us

News

Aƙalla Mutum Bakwai Ne Suka Rasu Bayan Da Wata Tirela Ta Murƙushe Motoci Biyu

Published

on

FB IMG 1759017479543

Aƙalla mutum bakwai ne suka rasu, yayin da wasu guda biyar suka ji rauni bayan wata tirela ta murƙushe motoci biyu a yankin Madalla, da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, a Jihar Neja.

Hatsarin ya auku ne da misalin ƙarfe 11:30 na safiyar ranar Juma’a, lokacin da wata tirela ta samu matsalar birki, ta yi awon gaba da wasu motoci biyu.

Advertisement

Yadda Sanata Barau Ke Samar Da Masana Don Cigaban Kano

Wani ganau, Saleh Haruna, ya ce kafin aukuwar hatsarin, direban wata motar bas ya bugi wata mota a gabansa, wanda hakan ya haddasa hatsaniya.

A cewarsa, a lokacin ne tirelar ta taho da sauri ta murƙushe su, hakan ya sa wani ɓangare na bas ɗin ya kama da wuta.

Advertisement

A sakamakon haka, mutum huɗu da ke cikin bas ɗin sun ƙone ƙurmus, yayin da sauran suka samu rauni.

An garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibitin Lukas da ke Madalla, inda Dakta Ugwoegbu Valentine, ya tabbatar da rasuwar ƙarin mutum uku daga cikin waɗanda suka ji rauni.

Advertisement

Direban tirelar, Sulaiman Rabiu, ya shaida cewa ya taso daga Warri, a Jihar Delta, yana ɗauke da buhun alkama waɗanda zai kai Kano.

Ya ce lokacin da yake saukowa daga Madalla ne birkin motarsa ya ƙi aiki, lamarin da ya janyo hatsarin.

Advertisement

Rundunar ’yan sandan yankin Madalla ta tabbatar da rasuwar mutum bakwai a hatsarin.

Sai dai jama’a a yankin sun koka kan yadda aikin gyaran hanyar Abuja zuwa Kaduna ke tafiya.

Advertisement

Sun zargi kamfanin da ke aikin da gazawa wajen saka alamomi da samar da wuraren tsayawar fasinjoji da motoci.

 

Advertisement

 

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending