News
Rundunar Sojin Najeriya Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Mai Garkuwa Da Mutane A Taraba
Rundunar sojin Najeriya ta cafke wani da ake zargin mai garkuwa da mutane, Umar Musa Geyi, a karamar hukumar Wukari yayin da yake tattaunawa kan kudin fansa na Naira miliyan 20 daga dangin wani da aka sace.
Kakakin rundunar, Laftanar Umar Mohammed, ya ce wanda ake zargin yana cikin jerin wadanda hukumomin tsaro ke nema, kuma yana da hannu a sace Alhaji Jano, wani Bafulatani mazaunin Jandei-Kulala, wanda aka sace ranar 13 ga Nuwamba, 2025.
Kare Kai Da Al’ummomi Ke Yi Ne Ke Kara Haifar Da Sabbin Rikice-rikice A Filato – Sojin Najeriya
“Laftanar Mohammed ya ce: ‘Binciken farko ya nuna wanda ake zargin yana da alaka da sace Alhaji Jano, kuma har yanzu yana hannun masu garkuwa.’”
Ya kara da cewa wanda ake zargin an kama shi ne yayin da ake tattaunawa da dangin wanda aka sace a kan kudin fansa na Naira miliyan 20, sannan yana hannun jami’an tsaro yanzu ana ci gaba da yi masa tambayoyi domin gano inda wanda aka sace yake.
Kwamandan 6 Brigade, Brigade General Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba wa sojojin kan jajircewa da kwarewarsu, tare da tabbatar da cewa rundunar tana ci gaba da yaki da duk wata kungiyar masu laifi a fadin jihar.
Rundunar ta ce za ta ci gaba da bincike domin kamo sauran da ke da hannu a wannan lamarin, tare da tabbatar da cewa wanda aka sace zai dawo hannun iyalansa lafiya.
