News
Wani Ya Kashe Ɗan Uwansa Saboda Ya Harbe Shi A Mafarki
An kama wani mutum mai shekaru 43 a duniya a garin Sepeteri na Jihar Oyo, bisa zargin kashe babban yayansa, Mustapha Amidu, bayan ya yi zargin ya harbe shi a mafarki.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Ayanlad Olayinka ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Ibadan.
Gwamnatin Jihar Kano Ta Kai Tallafi Ga Wadanda Gobara Ta Shafa a Garin Zago
Ya ce an kai rahoton lamarin hedikwatar ’yan sanda ta Ago-Amodu daga wani mutum mai suna Badmus Yunisa na unguwar Alegunlode a yankin Sepeteri.
A cewarsa, wanda ake zargin ya je inda marigayin yake zaune, ya ɗauki wani babban dutse ya buga masa a kai sannan ya tsere.
An garzaya da marigayin zuwa asibitin Ileri-Oluwa da ke Sepeteri, amma likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.
Olayinka, ya ce bayan samun rahoton, jami’an ’yan sanda ƙarƙashin jagorancin shugaban ofishin Ago-Amodu sun ziyarci wajen da lamarin ya faru da kuma asibitin domin fara bincike.
Ya ƙara da cewa an kama wanda ake zargin, kuma ya amsa laifin, yana kuma ba ’yan sanda haɗin kai wajen gudanar da binciken.
Ya kuma ce kwamishinan ’yan sandan jihar, Femi Haruna, ya bayar da umarnin a mik5a lamarin zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na jihar (SCID) domin ci gaba da bincike.
-
News6 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News6 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
