News
Jami’an NSCDC Sun Kama Matasa 4 Yayin Da Suka Fito Kwacen Wayoyin Masu Zuwa Tahajjud A Kano
Jami’an Tsaron Civil Defence a Jihar Kano sun kama wasu matasa hudu da ake zargi da tayar da tarzoma da kuma kwacen waya lokacin sallar Tahajjud a unguwar Dorayi Babba da ke Karamar Hukumar Gwale a Jihar Kano.
Wannan na kunshe ne ta cikin sanarwar da jami’in hulda da jama’a na rundunar a Kano SC Ibrahim Idris Abdullahi ya fitar a ranar Jumuʼa 13 ga Maris 2026.
Takaddamar Nukiliyar Iran Da Yammacin Duniya/Amurka Da Isra’ila: Za A Iya Samun Mafita?
Sanarwar ta ce jami’an hukumar sun kama matasan ne yayin sintiri bayan samun bayanin cewa wasu gungun matasa dauke da makamai suna kai hari ga masu gudanar da sallar Tarawihi da kuma masu wucewa a kusa da wata makaranta da ke Dorayi Babba.
Sanarwar ta ce jami’an sun fatattaki matasan tare da kama wasu daga cikinsu bayan sun kai hari ga wani mutum tare da kwace masa wayarsa.
Sanarwar ta kara da cewa bincike kan lamarin ya kammala kuma za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News5 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News4 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
